Fadar Shugaban Kasa ta ce a ranar Talata Shugaba Muhammadu Buhari zai sanya hannu a kan kasafin kudin shekarar 2023 da muke ciki.
Hadimin Shugaban Kasa Kan Kafofin Yada Labarai na Zamani, Bashir Ahmad, ya ce, Buhari zai sanya hannu kan kasafin ne a Fadar Shugaban Kasa.
Shugaban Kasa zai rattaba hannu kan kasafin ne bayan amincewar Majalisar Dokoki ta Kasa, wadda ta kara Naira tiriliyan 1.3 a kan abin da shugaban kasar ya gabatar mata na tiriliyan N20.5.
Sanya hannu kan kasafin na zuwa ne a ranar da aka dawo daga hutun bikin shiga Sabuwar Shekara.