Daga Maryam Sulaiman Muhammad
Shugaban hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), Dauda Ali Biu, ya bayyana alhininsa ga mutanen da hatsarin ya rutsa da su a hadarin jirgin kasa mai tafiya da kuma motar ma’aikatan jihar Legas a mashigar jirgin kasa na PWD da ke kan titin Agege, Legas ranar Alhamis. .
Rundunar ta Corps Marshal ta kuma gargadi hukumomin da abin ya shafa da su gina daidaikun kofofin layin dogo don inganta tsaro a ayyukan jiragen kasa a fadin kasar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in kula da ilimin jama’a na Corps, ACM ya sanarwa PRIME TIME NEWS. Bisi Kazeem.
Bisi ya bayyana cewa, Corp Marshal Yayin da ya kuma yin kira ga ‘yan kasuwa da su guji dabi’ar rashin kyau na siyar da kayan su a wajen.
A cewarsa, motar bas Marcopolo mai lamba 04A-48LA da ta yi hatsarin dauke da fasinjoji 85 daga ciki an tabbatar da mutuwar manya 2 da ke cikin motar a nan take yayin da 4 suka mutu daga baya a asibiti sannan an ceto sauran 79 da suka samu raunuka daban-daban. Yanzu haka suna karbar magani a asibitin koyarwa na jami’ar jihar Legas da ke Ikeja.
Biu ya jajantawa iyalan wadanda suka mutu sannan ya kuma yi fatan wadanda suka jikkata cikin gaggawar samun lafiya da kuma iyalan wadanda suka rasun su jajirce wajen jure asarar da aka yi.
Ya yabawa tawagar FRSC da duk masu kai daukin farko kamar ‘yan sandan Najeriya, LASEMA, LASTMA da suka yi gaggawar ceto wadanda lamarin ya rutsa da su, ya kuma yi alkawarin za a binciki hadarin.