Home » Gwamnatin Jihar Kano ta dage dokar hana Zirga- Zirga

Gwamnatin Jihar Kano ta dage dokar hana Zirga- Zirga

by Maryam Sulaiman Muhammad
0 comment 1 minutes read

 

Daga Maryam Sulaiman Muhammad

Gwamnatin jihar Kano ta dage dokar hana fita da ta sanya a jihar da nufin kaucewa tabarbarewar doka da oda biyo bayan bayyana sakamakon zaben gwamna da na ‘yan majalisar dokokin jihar.

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya sanar da dage dokar a cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Litinin.

Ya ce an dauki matakin dage dokar ne bayan an yi nazari sosai kan lamarin da kuma kwanciyar hankali da  ya kasance a jihar.

Kwamishinan ya yi kira ga bankunan kasuwanci da ma’aikatan gwamnati da sauran al’ummar jihar da su fito su ci gaba da sana’o’insu na yau da kullum.

You may also like

Leave a Comment

About Us

We are a media platform published by Prime Time Newspapers Limited, based in Kano. its committed to passionate, insightful and objective coverage on democracy, governance, business, security and humanitarian values.

Feature Posts

Newsletter

Subscribe my Newsletter for new blog posts, tips & new photos. Let's stay updated!

This website uses cookies to improve your experience. We'll assume you're ok with this, but you can opt-out if you wish. Accept Read More