Home » Mu Tashi Tsaye Domin Kawo Karshen Rikicin Sudan — Aisha Buhari

Mu Tashi Tsaye Domin Kawo Karshen Rikicin Sudan — Aisha Buhari

by Maryam Sulaiman Muhammad
0 comment 1 minutes read

Uwargidan Shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta roki a hada karfi da karfe don ganin kurar rikicin Sudan ta kwanta.

Jaridar Premium Times ta ruwaito Aisha Buhari na wannan kira a wani taro da ta jagoranta jiya Litinin a Fadar Gwamnati da ke Abuja.

A cewar jaridar, Aisha Buhari na ganin akwai rawar da matan shugabannin Afirka za su iya takawa musamman wajen kai agaji Sudan.

Tun ranar 15 ga watan Afrilu, yaki ya barke a Sudan kuma har wannan lokaci, an kasa cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin.

Sama da mutane 500 ake kyautata zaton cewa rikicin ya yi sanadin rasuwarsu kawo yanzu.

Mutum sama 700,000 sun rasa muhallansu

Alkaluman mutanen da rikicin Sudan ya raba da muhallansu ya ninka zuwa sama da mutum 700, 000, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Karuwar mutanen da ke guje wa muhallansu ya sanya fargaba kan yaduwar fadan duk da tattaunawar tsagauta bude wuta da ake yi a Saudiyya.

Khartoum na da al’umma kusan miliyan 5.4, sai dai an daidaita birnin mai cike da zaman lafiya a baya tun bayan barkewar fada a ranar 15 ga watan Afrilu.

Ana gudanar da fadan ne tsakanin sojojin kasar da Janar Abdel Fattah al-Burhan ke jagorata da kuma dakarun RSF bangaren Janar Mohamed Hamdan Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti.

Sama da mutum 600 ne aka kashe kawo yanzu tare da jikkata 5,000.

You may also like

Leave a Comment

About Us

We are a media platform published by Prime Time Newspapers Limited, based in Kano. its committed to passionate, insightful and objective coverage on democracy, governance, business, security and humanitarian values.

Feature Posts

Newsletter

Subscribe my Newsletter for new blog posts, tips & new photos. Let's stay updated!

This website uses cookies to improve your experience. We'll assume you're ok with this, but you can opt-out if you wish. Accept Read More