Home » Mun Gano Yadda Gwamnatin Ganduje Ta Karkatar Da Biliyan 100 Na Kananan Hukumomi – Muhyi Magaji

Mun Gano Yadda Gwamnatin Ganduje Ta Karkatar Da Biliyan 100 Na Kananan Hukumomi – Muhyi Magaji

by Salisu Hamisu Ali
0 comment 1 minutes read

Kwamitin karbar mulki na jam’iyyar NNPP a Kano ya bayyana yadda Gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta karkatar da kudin kananan hukumomi Biliyan 100.

Mamba a kwamitin dawo da kadarorin Gwamnati na babban kwamitin karbar mulkin na NNPP, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana hakan yayin wani taron karfafa samar da bayanai a bincike ta hanyar aikin jarida domin yaki da cin hanci da rashawa ta amfani da harsunan Najeriya yau Asabar a Kano.

Cibiyar WADATA da WAMAC da tallafin gidauniyar MacArthur ne suka shirya taron.

“Daftarin bayanai a hukumance da aka samu ya nuna yadda aka karkatar da kudaden kananan hukumomi Biliyan 10 daga asusun gwamnati zuwa na daidaikun mutane, wannan daban ne da irin badakaloli da binciken mu ya gano”, inji Muhuyi.

Haka kuma ya ce irin ayyukan cin hanci da rashawa dake cikin gwamnatin mai barin gado shi kansa bai san su ba sai da ya shiga kwamitin karbar mulkin.

You may also like

Leave a Comment

About Us

We are a media platform published by Prime Time Newspapers Limited, based in Kano. its committed to passionate, insightful and objective coverage on democracy, governance, business, security and humanitarian values.

Feature Posts

Newsletter

Subscribe my Newsletter for new blog posts, tips & new photos. Let's stay updated!

This website uses cookies to improve your experience. We'll assume you're ok with this, but you can opt-out if you wish. Accept Read More