Home » Zamu sa Ƴan Sanda su kama ka – Majalisa ta gargaɗi Gwamnan CBN Emefiele

Zamu sa Ƴan Sanda su kama ka – Majalisa ta gargaɗi Gwamnan CBN Emefiele

by Salisu Hamisu Ali
0 comment 1 minutes read

Shugaban majalisar Wakilan Najeriya, Femi Gbajabiama ya ce a shirye yake ya baiwa babban sufeto janar na ‘yan sandan Najeriya umarnin kama Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele domin sanya shi ya gurfana gaban majalisar.

Gbajabiamila ya bayyana hakan a yau Alhamis yayin da yake mayar da martani kan rahotan da shugaban kwamitin riko na majalisar da ta kafa dan shiga tsakanin Bankuna da babban bankin kasar karkashin jagorancin shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhassan Doguwa.

Doguwa ya shaidawa majalisar cewa Bankin CBN da Emifiele basu amsa gayyatar kwamitinsa ba a ranar Laraba.

Sai dai shugaban majalisar ya ce zai yi amfani da damar kundin tsarin Mulki ya bashi wajen baiwa ‘yan sanda umarnin kama Gwamnan Bankin domin tilasta masa ya gurfana gaban majalisar.

You may also like

Leave a Comment

About Us

We are a media platform published by Prime Time Newspapers Limited, based in Kano. its committed to passionate, insightful and objective coverage on democracy, governance, business, security and humanitarian values.

Feature Posts

Newsletter

Subscribe my Newsletter for new blog posts, tips & new photos. Let's stay updated!

This website uses cookies to improve your experience. We'll assume you're ok with this, but you can opt-out if you wish. Accept Read More